in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban ki-moon ya bukaci Koriya ta Arewa da ta yi kokarin tabbatar da burin cimma zaman lafiya da karko a zirin Koriya
2013-04-05 16:19:48 cri
A ranar 4 ga wata, sakatare janar na M.D.D. Ban Ki-Moon da ke yin ziyara a kasar Spain ya bayyana cewa, yana fatan Koriya ta Arewa za ta tashi tsaye don shiga yunkurin tabbatar da zaman lafiya da karko a zirin Koriya, inda kuma ya bukaci bangarorin da abin ya shafa da su yi kokari tare, ta hanyar yin shawarwari domin a warware halin kuncin da ake ciki.

A gun taron manema labaru da aka yi a wannan rana a birnin Madrid, Ban ki-moon ya ce, halin da ake ciki yanzu a zirin Koriya na ci gaba da tsananta, kuma muddin aka yi kuskure wajen yanke shawara game da halin da ake ciki a yankin, hakan na iya haddasa mummunan sakamako.

Sabo da haka, ya nuna fatan cewa Koriya ta Arewa za ta canja manufar da take bi kuma ta kai zuciya nesa. Ya ci gaba da cewa, bisa rahoto da aka samu game da harkokin tsaro da aikin jin kai da ake ciki a wurin, ana gani lamarin na iya kawo damuwa sosai.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China