in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta nuna rashin jin dadi kan sake farfado da tasoshin nukiliya na Koriya ta Arewa
2013-04-02 16:43:41 cri
A ranar Talata 2 ga wata, game da batun sake farfado da tasoshin mukiliya da kasar Koriya ta Arewa ta yi, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Hong Lei ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, Sin ta nuna rashin jin dadi kan wannan batu, don haka take kira ga bangarori daban daban da su yi hakuri, a kokarin komawa hanyar yin shawarwari tsakaninsu cikin sauri.

Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na kasar Koriya ta Arewa KCNA ya bayar a ranar 2 ga wata, mai magana da yawun babbar hukumar makamashin nukiliya ta kasar ya bayyana a ranar cewa, kasar za ta sake farfado da tasoshin nukiliya dake yankin Yongbyon.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China