in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Philippines ta mayar da martani ga yankin Taiwan
2013-05-15 14:33:20 cri
A ranar 14 ga wata da karfe 12 na dare, wa'adin karshe da yankin Taiwan na kasar Sin ya tsara ga gwamnatin Philippines don ta mayar da martani game da harin da ta kai ga jirgin ruwa mai kamun kifaye na Taiwan ya cika. A wannan rana da dare, wani jami'in ofishin kula da harkokin al'adu, da tattalin arziki, da cinikayya na Manila, da ke birnin Taipei, ya ziyarci sashen da batun ya shafa a yankin Taiwan, bayan da aka tattauna cikin siri har na awoyi da dama, a ranar 15 ga wata da sanyin safiya, wannan jami'i da wasu jami'ai daga yankin Taiwan sun shirya taron manema labaru tare.

Wani jami'i daga yankin Taiwan ya bayyana cewa, bayan da aka tattauna da dudduba wasikar da Philippines ta kawo, ana iya cewa, Philippines ta nuna bakin ciki tare da neman gafara game da kai hari kan jirgin ruwa na yankin Taiwan, sabo da haka, a iya cewa, Philippines ta mayar da martani kamar yadda yankin Taiwan yake bukata, amma, duk da haka, akwai saura-rina-a-kaba game da ci gaba da tabbatar da sauran batutuwa, musamman ma batun biyan kudin diyya.

Ya bayyana cewa, yankin Taiwan yana fatan gwamnatin Philippines za ta tsara matakai wajen biyan kudin diyya nan take, da yin alkawarin kaucewa sake aukuwar irin wannan lamari. Ya ci gaba da cewa, yankin Taiwan zai ci gaba da inganta tsaron masu kamun kifaye a wadannan wurare, kuma yanzu, ana ci gaba da ba da kariya ga masu kamun kifaye a wurin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China