in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar kishin Islama da ke gabashin kasar Turkistan, kungiyar 'yan ta'adda ce, in ji kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin
2013-11-26 16:30:36 cri
Yayin taron manema labaran da aka yi ran 25 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya bayyana cewa, hakika, kungiyar kishin Islama da ke kasar Turkista,kungiya ce ta ta'addanci, kuma kungiyar ta gabatar da wani hoton bidiyo, inda ta sanar da daukar alhakin harin da aka kai a filin Tian'an men ran 28 ga watan Oktoba, har ma ta yi barazanar cewa, za ta ci gaba da kai hare-haren ta'addanci a yankunan kasar Sin, lamarin ya nuna halin ta'addanci sosai na kungiyar, kuma ya sa mun gano gaskiyar harin da aka kai a ran 28 ga watan Oktoba.

Qin Gang ya bayyana haka ne yayin da ke amsa tambayoyin da manema labarai suka yi masa. Ya kuma bayyana cewa, MDD ta ayyana kungiyar kishin Islama ta gabashin kasar Turkistan a matsayin kungiyar 'yan ta'adda, cikin dogon lokaci da suka gabata, kungiyar ta kai hare-hare da dama a kasar Sin da sauran sassan duniya don cimma mummunan burinta wajen raba jihar Xinjiang daga kasar Sin, hare-haren da suka haddasa mutuwa ko jikkatar mutane da dama tare da kawo asarar dukiyoyi, sabo da haka, gwamnatin kasar Sin za ta ci gaba da daukar matakai masu tsanani wajen murkushe kungiyar.

Qin Gang ya jaddada cewa, ya kamata a yi yaki da kungiyoyin 'yan ta'adda bisa ka'ida daya, kuma ana bukatar hadin gwiwar kasa da kasa wajen gudanar da wannan aiki, bugu da kari, yaki da kungiyar kishin Islama ta gabashin kasar Turkistan ya kasance wani muhimmin aiki na hadin gwiwar kasa da kasa wajen yaki da kungiyoyin 'yan ta'adda. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China