in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kashe 'yan jaridar rediyon kasar Faransa RFI biyu a Mali
2013-11-03 16:26:10 cri
'Yan jaridar rediyon kasar Faransa RFI biyu da aka sace, an kashe a ranar Asabar a yankin Kidal dake arewa maso gabashin Mali, tashin hankalin da ya tura kasar Faransa da kasar Mali kara karfafa matakan yaki da kungiyoyin 'yan ta'adda a wannan kasa. A ranar Asabar ce, ministan harkokin wajen kasar Faransa ya tabbatar da mutuwar 'yan jaridar biyu na RFI, Ghislaine Dupont da Claude Verlon da mutane masu rike da makamai suka sace a Kidal da misalin kusan karfe daya na rana agogon wurin. A cewar labarin da RFI ta bayar a shafinta na yanar gizo, 'yan jaridar biyu an yi awon gaba da su a bakin kofar gidan Ambery Ag Rissa wani wakilin kungiyar neman 'yancin yankin Azawad na MNLA ta 'yan tawayen Abzinawa na Kidal.

A cikin wata hirarsa ta wayar tarho bayan hadarin, shugaban kasar Faransa Francois Holllande da takwaransa na kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita sun bayyana niyyarsu ta ci gaba yaki da kungiyoyin kishin islama dake arewacin kasar Mali.

A nasa bangare ministan harkokin wajen kasar Faransa ya yi alkawarin hada karfi da karfe tare da hukumomin kasar Mali domin gano dalilin mutuwar wadannan 'yan jarida. Shugaban diplomasiyyar kungiyar tarayyar Turai, Catherine Ashton ta bayyana bacin ranta matuka kan wannan kisan gilla tare jaddada goyon bayan kungiyarta ga kasar Mali game da kokarin da take na yaki da ta'adanci. Haka kuma a kasar Mali jam'iyyun siyasa da na kungiyoyin fararen hula a inuwar kawancen FDR domin yin allawadai da wannan kisa tare da yin kira ga hukumomin kasar su dauki matakan da suka wajaba kan matsalar ta'adanci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China