in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 23 ne suka mutu a sakamakon hare-haren ta'addanci a Iraki
2013-11-24 16:46:04 cri
A ranar Asabar 23 ga wata, mutane 23 ne suka mutu, yayin da wasu 95 suka jikkata a sakamakon fashewar boma-bomai da harbe-harbe da aka yi a Iraki, in ji 'yan sandan kasar.

Wani mai samun sako daga 'yan sandan kasar Iraki ya bayyana cewa, a yankin Tuz Khourmatu dake da tazarar kilomita 170 daga Baghdad a arewa, an kai jerin hare-haren boma-bomai na kunar bakin wake a cikin mota da kuma gefen hanya a kusa da wani masallaci na darikar Shia a daren Asabar, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane 12, yayin da wasu 72 suka jikkata. Yankin Tuz Khourmatu na kasancewa a arewa maso gabashin jihar Salaheddin, inda Larabawa, kurdawa, da kuma 'yan Turkmen suke zama tare. Lamarin dake janyo rikicin addini lokaci zuwa lokaci tsakanin al'ummomi mazauna wurin, haka kuma yankin na fama da hare haren ta'addanci a kai a kai.

Ban da haka, a wannan rana, an yi harbe-harbe sau da dama a birnin Baghdad, da Tal Afar dake arewa maso yammacin Baghdad, da birnin Baqouba, hedkwatar jihar Diyala dake gabashin kasar, da kuma birnin Mosul, hedkwatar jihar Nineveh dake arewacin kasar Iraki, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane da kuma jikkata wasu da dama.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China