in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu ko ji rauni a sakamakon harin ta'addanci da ya auku a kasar Iraki ya kai 290
2013-08-11 16:17:22 cri

'Yan sandan kasar Iraki sun bayyana a ranar 10 ga wata cewa, an samu hare-haren ta'addanci a wurare daban daban dake kasar, ciki har da Bagadaza, babban birnin kasar, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla 40, yayin da kuma wasu 250 suka ji raunuka.

Kasancewar hare-haren sun auku ne a ranar bikin Karamar Sallah, lokacin da jama'a da dama ke gudanar da bukukuwa, hare-haren sun haddasa rasa rayuka da raunatar mutane da dama.

Tun farkon wannan shekarar ta bana, ake ta samun hare-haren ta'addanci a kasar Iraki, wadanda suka kawo babbar illa ga zaman lafiya a kasar. Bisa kididdigar da tawagar MDD dake kasar Iraki ta yi a kwanakin baya, an ce, a sakamakon hare-haren da aka kai wa kasar Iraki a watan Yulin bana, mutane 1057 ne suka mutu, baya ga wasu 2326 da suka ji raunuka, don haka wannan wata ya kasance watan da aka fi samun mutuwa da raunatar mutane a cikin shekaru 5 da suka gabata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China