in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar sabon zagayen tattaunawa game da batun nukiliyar kasar Iran.
2013-11-21 15:15:40 cri
An kaddamar da sabon zagayen taron tattaunawa game da batun nukiliyar kasar Iran, a ranar 20 ga watan nan wanda aka shafe kwanaki 3 ana yin sa a birnin Geneva, bayan da aka kasa cimma matsaya guda a yayin taron tattaunawa a karo da ya gabata.

Ana sa ran wakilai daga kasashen Amurka, da Rasha, da Sin, da Faransa, da Birtaniya, da Jamus, da kuma Iran za su ci gaba da kokarin daddale yarjejeniya kan wannan batu a wannan karo.

A wannan rana, bayan da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin, da firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu suka kammala shawarwari tsakaninsu, shugaba Putin ya fada wa kafofin yada labaru cewa, Rasha na farin ciki da ganin an kaddamar da taron tattaunawar na wannan lokaci.

Har ila yau wani jami'in diplomasiyyar kasar Amurka ya bayyana a wannan rana cewa, sai a daddale yarjejeniya daga dukkan fannoni game da batun nukiliyar kasar ta Iran kawai, kasashen yammacin duniya za su iya soke takunkumin da suka kakabawa kasar.

Shi ma a jawabin sa na wannan rana, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Li Baodong, ya bayyana cewa, an gudanar da shawarwari a karon da ya gabata cikin tsanaki, kuma bangarori daban daban, sun bayyana aniyyar su, ta warware batun nukiliyar kasar Iran ta hanyar yin shawarwari a siyasance.

Yace an riga an cimma matsaya guda a wasu muhimman fannoni, kuma dukkan sharuddan da aka cimma sun zamo wani muhimmin harsashi ga ci gaba da yin shawarwarin a wannan karo.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China