in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya bukaci a kara aiwatar da gyare-gyare a bana
2013-11-14 12:32:39 cri
A ranar 13 ga wata ne, firaministan kasar Sin Li Keqaing ya shugabanci zaunannen taron majalisar gudanarwa, inda ya tsara aikin kara fahimta da aiwatar da abubuwan da aka tattauna a yayin taron cikakken zama na 3 na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18, kuma ya bukaci da a kara aiwatar da gyare-gyare a wannan shekara, da karfafa aikin yin gyare-gyare daga dukkan fannoni, don inganta da samar da daidaito a aikin raya tattalin arziki da zamantakewa cikin dogon lokaci.

A gun taron, an bayyana cewa, yayin taron cikakken zama na 3 na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18, an tsara shirin karfafa aikin yin gyare-gyare daga dukkan fannoni zuwa wani lokaci a nan gaba. Wajibi ne hukumomi na matakai daban daban su bi manufar da aka cimma a yayin taron, da daukar hakikanin matakai, don kara aiwatar da gyare-gyare, da sa kaimi ga raya tattalin arziki yadda ya kamata, ta yadda jama'ar kasar za su kara ci moriyar sakamakon gyare-gyare da raya kasa da aka samu.

A gun taron, an bayyana cewa, domin kara aiwatar da gyare-gyare, dole ne a cika alkawarin da aka dauka wajen inganta aikin yin gyare-gyare da karfafa zukatan jama'a game da aikin yin gyare-gyare, don aza wani harsashi wajen gudanar da wannan aiki, da duba yadda aka aiwatar da manufar, ta yadda za a kara himma wajen aiwatar da gyare-gyare daga fannoni daban-daban, kuma a samu sakamakon gyare-gyaren a kai a kai.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China