in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta zama mambar hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD bisa kuri'u da yawa da ta samu
2013-11-13 20:31:08 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Mista Qin Gang ya bayyana a gun taron manema labaru da aka shirya a ran laraba 13 ga wata cewa, a ranar Talata nan 12 ga watan Nuwamba, aka zabi kasar Sin ta zama mambar hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD na wa'adin shekaru uku.

Sin dai na daya daga cikin kasashe 14 bisa kuri'u mafi rinjaye da ta samu, a yayin babban taro karo na 68 na MDD, kuma wa'adin aikinta zai fara ne daga shekara ta 2014 zuwa ta 2016.

Qin ya yi bayanin cewa, wannan zaben ya nuna cewa, kasashen duniya sun amince da kyakkyawan sakamakon da Sin ta samu na raya sha'anin hakkin dan Adam, da kuma mu'ammala da cudanya da kasar Sin take yi cikin yakini tare da sauran kasashen duniya.

Don haka kasar Sin ta nuna godiya ga dukkan kasashen da suka zabi ta na zama mambar hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD.(Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China