in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a ci gaba da shawarwari kan batun nukiliyar kasar Iran a birnin Geneva
2013-11-09 17:28:55 cri
A ci gaba da dukufa da bangarori daban daban ke yi wajen cimma ra'ayi daya, a Asabar din nan ake ci gaba da taron shawarwari kan batun nukiliyar kasar Iran na wannan zagaye a birnin Geneva, wanda bisa shirin da aka tsara, ya kamata a kammala taron a jiya Jumma'a 8 ga wata.

A ranar 7 ga wata, wakilan kasashe shida masu ruwa da tsaki kan batun nukiliyar kasar ta Iran, watau Amurka, Burtaniya, Faransa, Rasha, Sin da Jamus da wakilin kasar ta Iran sun fara wani sabon zagaye na yin shawarwari tsakaninsu wanda bisa jadawalin da aka tsara, za a kammala cikin kwanaki biyu. Sai dai bayan kammala shawarwari a ranar ta daya, ta bakin kakakinta, babbar wakiliya mai kula da harkokin waje da manufofin tsaro ta tarayyar kasashen Turai Catherine Ashton ta bayyana cewa, a halin yanzu, kasashe shida da kasar Iran na dukufa wajen tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran din, tana kuma fatan za a iya samun ainihin ci gaba kan batun, idan har kasar Iran din za ta iya yin alkawari, da zai baiwa watakila kasashe shida damar sa hannu kan yarjejeniyar da za a cimma.

Yayin da ake ci gaba da tattaunawa a hannu guda a ran 8 ga wata, firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ba da wata sanarwa, da ke kunshe da nuna matukar kiyayarsa ga dukkan yarjejeniyoyin da kila kasashe shida za su kai ga sanyawa hannu yayin taron shawarwarin da ake yi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China