in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kananan manoma zasu iyar taimakwa wajen yaki da karancin abinci a kasar Afrika ta Kudu, in ji wani masani
2011-07-15 10:43:38 cri
Kananan manoma na da wani muhimmin matsayi wajen yaki da karancin abinci idan suna samun jari mai kyau, tsare-tsaren cigaba, da samar da manufar gwamnati da ta dace a wannan fanni, a cewar wani shugaban wata kungiyar cigaban manoma ta kasar Afrika ta Kudu a ranar Alhamis.

Gareth Ackerman, shugaban kungiyar "Pleiad Foundation" ya shaidawa kamafanin hadin gwiwar dillancin labarai na Afrika ta Kudu na SAPA cewa, kananan manoma zasu iyar kawo taimako sosai wajen kawar da matsalar karancin abinci da talauci a duniya.

A ranar Alhamis, kungiyar ta bada sanarwar fitar da wani sabon tsari dake da manufar taimakawa wajen shigar da kananan manoma dake gundumar Limpopo a kasar, ta yadda za'a samu wata hanyar kara samar da abinci.

Haka kuma kungiyar na bukatar bunkasa kwarewar manoman cikin tsarin kula, samar da abinci da kuma harkokin da suka shafi hukumar noma domin basu damar samun kudin shiga da na jari.(Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China