in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na sa kaimi ga baki 'yan kasuwa da su zuba jari kan sana'ar hako ma'adinai
2013-11-03 16:33:55 cri
A ran 3 ga wata, Mr. Jiang Daming, ministan kula da filaye da albarkatun kasar Sin ya bayyana a birnin Tianjin, cewar kasar Sin za ta kara bude kofarta da hadin gwiwa da kasashen waje a fannin bunkasa sana'ar yin amfani da filaye da hako ma'adinai, wato za ta sa kaimi ga baki 'yan kasuwa da su zuba jari a fannonin bincike da hako da kuma yin amfani da ma'adinai domin morewar damar samun ci gaba tare.

Jiang Daming ya kara da cewa, gwamnatin kasar Sin na mai da muhimmancin sana'o'in dake da nasaba da ma'adinai ga ci gaban tattalin arzikin kasar. A 'yan shekarun baya, kasar Sin ta kammala ayyukan bincike da dudduba ma'adinai iri 25, ciki har da karafe-karafe, tagulla da dai makamatansu. Bugu da kari, ta gano wasu muhimman filayen adanar man fetur, man gas, kwal da fadin kowanensu yake da girma sosai. Sannan yawan ma'adinan da kasar Sin za ta iya samar a kowace shekara ya kai ton kusan biliyan 10 daga ton biliyan 6.8.

A lokacin da ake namijin kokarin farfado tattalin arzikin kasa da kasa, mr. Jiang Daming ya shawarci masu tafiyar da harkokin ma'adinan halittu da su yi hangen nesa su yi kokarin bunkasa sana'o'in ma'adinan halittu cikin hadin gwiwa. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China