in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban babban taron MDD ya yaba ma kasashe masu bunkasuwa cikin sauri kan kokarinsu na kiyaye muhalli
2013-11-02 17:12:40 cri
Shugaban babban taron MDD John William Ashe ya ce, kasar Sin, da sauran kasahen dake samun saurin bunkasuwa ta fuskar tattalin arziki suna taka muhimmiyar rawa a kokarin tallafawa kasashe masu tasowa, na ganin sun sauya salon tattalin arzikinsu zuwa wanda zai dace da matakan kiyaye muhalli. Ashe ya bayyana hakan ne ga manema labaru bayan kammala taron baje kolin hadin gwiwar kasashe masu tasowa don samun ci gaba a Jumma'a 1 ga watan nan na Nuwamba.

A cewarsa, kasar Sin na kan gaba, wajen samar da gudummowa da yin hadin gwiwa da kasashe masu tasowa, don haka ta ba da taimako kwarai wajen tabbatar da ganin irin wadannan kasashe sun samu ci-gaba mai dorewa a nan gaba.

Haka zalika, Ashe ya kara da cewa, hadin kan kasahen dake samun saurin bunkasuwa a fannin na tattalin arziki a bangarorin cinikayya, da zuba jari, da musayar fasahohi ya kara habaka kokarin kasashe masu tasowar, wajen sauya salon tattalin arzikinsu. Ya ce, duk da cewa irin wadannan kasashe na fuskantar matsalolin da suka hada da talauci, da karancin abinci da tsaftataccen ruwa, da matsalar makamashi, da dai sauransu, a hannu guda matakan da suke dauka na amfani da sabbin fasahohi, da zuba jari, da gudanar da nagartattun manufofi za su sanya su samun damar warware matsalolin nasu yadda ya kamata. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China