in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya jaddada raya hulda a tsakanin Sin da kasashen Afirka
2013-10-17 20:47:25 cri
Ranar Alhamis 17 ga wata da yamma, a nan birnin Beijing, hedkwatar kasar Sin, Li Keqiang, firaministan kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Tanzaniya Mizengo Pinda, wanda ya zo halartar taron baje koli na yammacin kasar Sin karo na 14.

A yayin ganawar, mista Li ya nuna cewa, har kullum kyautata hadin gwiwar abokantaka a tsakanin Sin da kasashen Afirka, muhimmiyar manufa ce ga kasar Sin. A cikin sabon halin da ake ciki, kasar Sin na son hada kai da kasashen Afirka wajen yin amfani da kyakkyawar dama da daidaita kalubaloli tare, a kokarin samar da yanayi na zaman lafiya da kwanciyar hankali wajen tabbatar da samun bunkasuwa, da kuma kara raya huldar abokantaka irin na sabon salo a tsakanin Sin da Afirka bisa manyan tsare-tsare.

A nasa bangaren kuma, mista Pinda ya ce, Tanzaniya tana gode wa kasar Sin bisa goyon bayanta kan harkokin bunkasuwar Afirka cikin lumana. Don haka kasarsa na son inganta hadin gwiwa a tsakaninta da kasar Sin bisa tsarin taron dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka, a kokarin taka rawa wajen bunkasa dangantaka a tsakanin Afirka da Sin. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China