in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kafa tsarin bincike kan illar da gurbatacciyar iska ke haddasawa ga lafiyar al'umma
2013-10-29 15:16:38 cri

Ranar 28 ga wata, kwamitin kula da harkokin kiwon lafiya da kayyade haihuwa na kasar Sin, ya gabatar da "shirin aiwatar da bincike kan illar da gurbatacciyar iska ke haddasawa ga lafiyar al'umma na shekatar 2013", inda ya bayyana cewa, nan da shekaru 3 zuwa 5 masu zuwa, za a kafa wani tsarin bincike kan illar da gurbatacciyar iska ke haddasawa ga lafiyar al'umma a dukkanin fadin kasar Sin.

Bisa wannan shiri, an ce, a bana, za a fara aikin bincike kan illar da gurbatacciyar iska ke haddasawa ga lafiyar mutane a wasu wurare na larduna 16, wadanda suka fi fama da matsalar gurbatacciyar iska. Binciken da za a yi ya hada da nazari kan yawan mutuwar mutane, da kuma hadurran da su ke shafar lafiyar mutane, irin wadanda gurbatacciyar iska ke haddasawa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China