in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ECOWAS na kan hanyar kafa wata gamayyar harkokin kwastam
2013-10-27 17:01:18 cri
Kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS ta sanya hannu kan wani farashin harajin kwastam na hadin gwiwa dake bayyana wani muhimmin takin farko na kafa wata gamayyar kwastam, tare da bayyana niyyarta na tattauna yarjejeniyoyin dangantakar tattalin arziki na APE tare da kungiyar tarayyar Turai, ta yadda za'a samu wata dangantakar moriyar juna.

Wadannan matakai biyu sun kasance mafi muhimmanci da aka cimma a kwanakin da suka gabata a yayin zaman taron musamman a birnin Dakar da ya maida hankali kan batutuwan tattalin arziki.

Cimma farashin harajin, da zai fara aiki a ranar daya ga watan Janairun shekarar 2015 na bude hanya kan kafa wata gamayyar harkokin kwastam dake kunshe da kasashen mambobi goma sha biyar na kungiyar ECOWAS.

Haka kuma tare da cimma wannan farashin, an samu wani dandalin kasuwanci mai karfi na yin gogayya, da zai iya kawowa kungiyar ECOWAS wani babban taimako a cikin harkokin musanyar kasuwancin duniya da kuma bunkasa kasuwanci tsakanin al'ummomi, in ji shugaban kasar Cote d'Ivoire Alassane Ouattara, wanda ya kasance shugaban kungiyar ECOWAS a wannan karo.

Farashin nan wanda adadinsa aka yi hasashen cewa zai iya karuwa da kashi 35 cikin 100, za'a aiwatar da shi kan dukkan kayayyakin dake fitowa daga kasashen wajen shiyyar da zasu shiga a cikin yankunan kwastam na kungiyar ECOWAS. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China