in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana kokarin kula da batun sauyin yanayi, in ji kafofin yada labaran Birtaniya
2013-10-26 17:38:07 cri
Kafar yada labaran kasar Birtaniya ta BBC ta sanar da sakamakon wani binciken da aka gudanar, wanda ya shaida cewa, jama'ar kasar Sin suna sahun gaba a fannin fahimtar lamuran da suka shafi sauye-sauyen yanayin duniya, kana sun fi kokarin tinkarar wannan matsala, idan an kwatanta su da sauran al'ummun kasashen Asiya.

Sashin kula da ayyukan kafofin yada labarai na BBCn ne ya dauki nauyin wannan bincike, wanda ya shafi mutane kimanin dubu 33, dake kasashen Asiya 7, da suka hada da Sin, da India, da Pakistan, da dai sauransu. Sakamakon binciken ya sheda cewa, bayan da aka yi musu tambayoyi, yawan jama'ar kasar Sin da suka fahimci ma'anar kalmar 'sauye-sauyen yanayi' ya kai kashi 86%, kana yawan mutanen da suka yarda da abkuwar sauye-sauyen yanayi ya kai kashi 78%, alkaluman da suka fi wadanda aka samu a sauran kasashe 6.

Har wa yau kuma, da yawa daga cikin jama'ar kasar Sin da suka amsa tambayoyin, sun bayyana amfani da kyakkyawan tsarin kafofin zirga-zirgar jama'a, da makamashi mai tsabta, a matsayin hanyoyin warware matsalar sauyin yanayi. Kana a ganin wadannan jama'ar kasar Sin, babbar manufar da kasarsu ta dauka don tinkarar matsalar ita ce, kyautata fasahar yin amfani da makamashi. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China