Bisa labarin da aka bayar, an ce, a ranar Talata 22 ga wata, shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir da takwaransa na kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir Mayardit sun yi shawarwari da gabatar da wata sanarwa a birnin Juba, inda suka cimma daidaito kan batun gaggauta gina yankin iyakar kasa da ba na soja ba da batun Abyei da dai sauransu.
Game da wannan, Hua ta bayyana cewa, kasar Sin tana fatan kasashen Sudan da Sudan ta Kudu za su ci gaba da warware matsalolinsu ta hanyar yin shawarwari cikin lumana bisa ka'idar fahimtar juna. Kana Sin za ta ci gaba da yin kokari tare da kasa da kasa wajen kyautata da inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. (Zainab)