in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a tafiyar da harkokin yin gyare-gyare daga dukkan fannoni a cikakken zaman taro na uku karo na 18
2013-10-23 20:45:32 cri
Yau Talata 23 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a birnin Beijing cewa, Sin za ta yi nazari kan harkokin yin gyare-gyare daga dukkan fannoni da kuma tafiyar da shirye-shiryen gudanarwar gyare-gyare a wani sabon cikakken zama karo na 18.

Shugaba Xi Jinping ya kuma bayyana cewa, ya kamata a mai da hankali kan dangantakar da ke tsakanin yin gyare-gyare, neman bunkasuwa da kuma tabbatar da kwaciyar hankali, don ci gaba da 'yantar da tunanimmu, raya karfin samar da kayayyakin zaman takewar al'umma da kuma karfafa ayyukan kirkire-kirkire.

Shugaban kwamiti mai ba da shawara na kwalejin koyon ilimin gudanar da harkokin tattalin arziki na jami'ar Qinghua, kuma shugaban kamfanin Carlyle David M.Rubenstein da kuma shugaban majalisar cibiyar nazari ta Brookings na birnin Washington John L.Thornton sun ba da jawabi yayin ganawarsu da Mr. Xi, inda suka nuna imani cewa, kasar Sin na da kyakkyawar makoma, don haka, suna son ci gaba da karfafa ayyukansu a Sin, ta yadda za su ba da gudumawa ga bunkasuwar tattalin arziki da ayyukan ba da ilimi a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China