in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya kammala ziyarar aikinsa a kasar Malaisiya cikin nasara
2013-10-05 17:03:16 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya baro kasar Malaisiya ranar Asabar tare kama hanya zuwa tsibirin Bali na kasar Indonesiya domin halarta dandalin karo na 21 na shugabannin kasashen kungiyar hadin kai a fannin tattalin arziki a Asiya da yankin tekun Pasific, tare da kammala ziyararsa a kasar Malaisiya cikin nasara.

A yayin wannan ziyara tasa ta kwanaki biyu, mista Xi ya samu tattaunawa tare da shugabannin kasar Malaisiya, da yin musanyar ra'ayi bisa manyan batutuwan da suka shafi shiyoyi da kasa da kasa, da kuma shata makomar cigaban hulda tsakanin kasar Sin da Malaisiya.

Haka zalika shugabannin sun halarci bikin sanya hannu kan wasu jerin yarjeniyoyi na moriyar kasashen biyu.

Mista Xi da faraministan kasar Malaisiya Najib Razak sun dauki niyyar daukaka dangantakarsu bisa tushen huldar cin gajiya daga dukkan fannoni tare da kuma cimma yarjejeniya kan burin bunkasa yawan kasuwanci tsakanin kasashen biyu zuwa dalar Amurka biliyan 160 nan da shekarar 2017.

Jaridar kasar Malaisiya New Straits Times ya nuna a kan shafinta na farko a ranar Asabar cewa yarjejeniyoyin da aka cimma a yayin wannan ziyara ta Xi sun bude wani sabon babi na kara karfafa dangantaka tsakanin kasashen biyu.

Kasar Malaisiya ita ce kasa ta biyu, ban da Indonesiya, a yankin Asiya dake Kudu maso gabas, da Mista Xi Jinping ya kai ziyara a wannan karo. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China