in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sudan na burin ganin shigowar kasar Masar sosai cikin huldar dake tsakanin Sudan ta kudu da Sudan
2013-04-05 10:15:37 cri
Shugaban kasar Sudan Omar Al-Bashir ya yi kira ga kasar Masar ranar Alhamis cewa kasar ta kara yin tasiri wajen warware rikici dake tsakanin Sudan da Sudan ta kudu.

Yayin ganawa da shugaba Mohammed Morsi wanda ya iso birnin Khartoum a safiyar ranar a ziyarsa ta farko zuwa kasar Sudan bayan hawa kujerar mulki, Al- Bashir ya bayyana cewa suna fatan ganin kasar Masar ta zamo mai muhimmin tasiri a batutuwa da suka shafi yankin da ma duniya, don haka yake neman ganin kasar Masar ta zamo muhimmiya kan batun dangantaka tsakanin Sudan da Sudan ta kudu.

Da yake magana shugaba Morsi ya ce, Masar za ta mara bayan yunkurin kasashen Sudan da Sudan ta kudu wajen warware batutuwa da suke takaddama a kansu domin a cimma zaman lafiya da dorewa, inda ya yi alkwarin ba da dukkan wata gudummawa da za ta inganta tattaunawa tsakanin Khartoum da Juba. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China