in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Alhazan Najeriya za su fara dawowa gida a yau Lahadi
2013-10-20 20:22:42 cri

Tawagar farko dake kunshe da alhazan Najeriya 1000 za ta sauka dawo gida a ranar yau Lahadi 20 ga wata bayan kammala aikin Hajjin bana a kasar Saudiyya.

Alhazan jihohin Kwara, Ogun, Osun da Oyo ne za su fara isowa a ranar yau din, wadanda tun farko su ne suka fara tashi zuwa kasar ta Saudiyya a ranar 14 ga watan Satumban da ya gabata.

Hukumar aikin hajji ta kasar Najeriya wato NAHCON ta tabbatar da cewa za'a kammala jigilar dawowar alhazan tare da kayayyakinsu cikin wata daya.

Alhazai dubu saba'in da biyar ne daga Najeriya suka sauke farali a shekarar bana, ciki har da dubu 10 wadanda suka je ta jirgin yawo. (Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China