in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan jihar Edo a Najeriya sun amince da hukuncin kisa ga masu garkuwa da mutane
2013-10-19 20:33:48 cri
Gwamnatin jihar Edo dake kudancin tarayyar Najeriya ta amince da dokar data tanaji yankewa masu yin garkuwa da mutane hukuncin kisa.

Dokar a cewar gwamnan jihar ta Edo Adams Oshiomhole, ta biyo bayan gyaran fuskar da akaiwa dokar haramta yin garkuwa da mutane ta shekarar 2009 ne. Gwamna Oshiomhole ya ce wannan doka ta tanaji hukunci kisa ga wanda ya aikata, ko ya taimakawa masu garkuwa da mutane ta ko wace irin hanya.

Yace an kafa wannan doka ne duk kuwa da tarin kalubalolin dake tattare da aiwatar da ita, domin dakile mummunar sana'ar sace mutane dake ciwa al'ummar jihar tuwo a kwarya.

Daga nan sai Oshiomhole ya yi kira da matasan jihar da su kauracewa wannan mummunar sana'a, wadda a cewar sa ba zata taba zama halastacciyar hanyar neman arziki ba.(Saminu Alhassan Usman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China