in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutane da suka mutu a hadarin jirgin saman da ya faru a Najeriya ya kai 9
2013-10-03 20:23:59 cri
Hukumar bayar da agajin gaggawa a Najeriya, ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin a ranar Alhamis 3 ga watan oktoba cewa,yawan wadanda suka mutu bayan da wani karamin jirgin sama ya fadi a kusa da filin sauka da tashin jiragen sama na Murtala Mohammed na kasa da kasa da ke Lagos a kudu maso yammacin kasar ya karu zuwa 9.

Mai magana da yawun hukumar ta NEMA Ibrahim Farinloye, ya tabbatarwa Xinhua cewa,an gano gawawwaki 9 a wurin da hadarin ya faru,yayin da mutane 6 suka ritsa da rayukansu

Wata sanarwa da Xinhua ta samu ta ruwaito,janar manajan hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Lagos(LASEMA) Femi Oke-Osanyintolu na cewa, mutane 11 ne suka mutu a hadarin kana mutane 4 suka ritsa da rayukansu

Wasu majiyoyin hukumar kula da zirga-zirgar jiragen saman kasar, sun bayyana cewa,jirgin yana dauke da gawar tsohon gwamnan jihar Ondo ne Olusegun Agagu a kan hanyarsa ta zuwa Akure, babba birnin jihar, kafin ya fadi a Lagos.

Kakakin hukumar ta NEMA,ya bayyana cewa, hukumar na gudanar da bincike game da musabbabin hadarin. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China