in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar WFP ta kaddamar da shirin "kin cin abinci har na tsawon sa'o'i 24" na shekarar 2013
2013-10-16 17:06:54 cri
Yau Laraba 16 ga wata ita ce ranar abinci ta duniya. A wannan rana a nan birnin Beijing, an kaddamar da shirin "kin cin abinci har na tsawon sa'o'i 24"na shekarar 2013 da hukumar shirin samar da abinci ta duniya wato WFP ta kira.

A yayin gudanar da shirin, ban da birnin Beijing, biranen Guangzhou, Kunming, Changchun, Urumqi, Zhengzhou da sauran wurare su ma sun gudanar da shirin, inda masu aikin sa kai za su yi musayar bayanai da sauran jama'a game da matsalar yunwa. Bangaren da ke daukar nauyin shirin ya yi hasashe cewa, yawan mutane da za su halarta zai kai fiye da miliyan 30.

Bisa sabon rahoton da MDD ta gabatar, an ce, a halin yanzu akwai mutane kimanin miliyan 842 a duniya da suka dade suna fama da matsalar yunwa, kana yawan kananan yara wadanda yawan shekarunsu bai kai 5 ba da suka mutu sakamakon rashin abinci a kowace shekara ya kai miliyan 5.

"Kananan yara dake fama da matsalar yunwa da rashin abinci mai gina jiki za su fuskanci matsaloli da dama, ban da lafiyarsu, za su fuskanci matsaloli a makaranta har ma a wuraren aiki a nan gaba.", a cewar wakilin hukumar WFP dake kasar Sin Huang Ansheng. Kana ya kara da cewa, don warware matsalar, ana bukatar jama'a da su yi hadin gwiwa tare da shiga a dama da su don warware matsalar a duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China