in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a taimakawa kasashen dake yamma da tsakiyar Afrika wadanda suke fama da karancin abinci
2012-05-07 14:20:07 cri
Ranar Lahadi 6 ga wata a birnin Geneva, hukumar abinci ta duniya wato WFP da hukumar 'yan gudun hijira ta MDD sun yi kira ga wasu kasashen duniya da su mai da hankali kan kasashen dake yamma da tsakiyar Afrika wadanda suke fama da karancin abinci mai tsanani.

WFP ta ba da sanarwa a wannan rana cewa, wadannan kasashe sun fuskanci bala'in fari a bana, abin da ya sa miliyan mutane su na fama da yunwa. WFP da hukuma mai kula da 'yan gudun hijira, suna fatan kasashen duniya da su kara samar da kudi domin sayen abinci ga wadannan kasashe.

WFP ta ce, alal misali, bala'in fari da aka fuskanta a kasar Nijar ya kawo illa ga aikin gona, abin da ya haifar da hauhawar farashin amfanin gona, har ma ana fuskantar karancin hatsi. Yawan jarirai da suke da watanni shida zuwa 23 da haifuwa na fama da karancin abinci mai gina jiki. A cikin watanni shida da suka gabata a bana, WFP ta samarwa 'yan kasar Nijar sama da miliyan 1 abinci, ban da wannan kuma, WFP na shirin ci gaba da samarwa kasar abinci daga watan Yuni zuwa na Satumba.

Dadin dadawa, WFP ta ce, jami'in hukumar da wani babban jami'in na hukumar 'yan gudun hijira ta MDD sun tafi kasar domin sa ido kan halin da ake ciki a kasar ta Nijar. Wadanda kuma, sun sa ido kan shirin da WFP ta yi kan jama'ar wurin na shiga aikin gine-ginen more rayuwa domin samun abinci.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China