in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin DRC ta soki harbar da kungiyar M23 ta yi a kan jirgin saman MONUC
2013-10-15 11:02:44 cri
Ran 14 ga wata, gwamnatin jamhuriyar demokuradiyar kasar Congo DRC ta yi suka mai tsanani kan kungiyar adawa da gwmanati ta M23 don gane da harba wani jirgin sama na kungiyar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake kasar MONUC, tana mai kira ga gamayyar kasa da kasa da ta dauki  mataki a kan.

A wannan rana, kakakin gwamnatin kasar Lambert Mende ya bayyana cewa, babu shakka harbar da kungiyar M23 ta yi a kan jirgin saman kungiyar MONUC ta saba da dokar kasa da kasa, kuma bisa ka'idojin yarjejeniyar Geneva da karin bayaninta, ana iya yanke mata hukuncin laifin yaki. Don haka Mr. Mende ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa da ta dauki matakin da ya wajaba domin kiyaye matsayin MDD.

Ran 12 ga wata, kungiyar adawa ta M23 ya amince da daukar alhakin harbo wani jirgin sama mai saukar ungulu na kungiyar MONUC bisa dalilin cewa, wannan jirgin sama bai bi hanyar da ta dace ba. Amma Mr. Mende ya ce, DRC ba ta hana jiragen saman kungiyar MONUC su shiga cikin sararin saman kasar ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China