in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar MDD ta yi kiran da a kwantar da hankali bayan sake barkewar wani fada a Gabashin Jamhuriyar demokuradiyyar Congo
2013-07-23 15:11:07 cri
Tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD(MONUSCO) ta bayar da rahoton cewa, wani mummunan fada ya sake barkewa ranar Litinin tsakanin sojojin kasar ta Congo da kuma dakarun kungiyar nan ta M23 da ke dauke da makamai a Mutaho-Kibati kusa da Goma da ke lardin arewacin Kivu.

Kakakin MDD Martin Nesirky ne ya bayyana hakan a taron manema labarai, inda tawagar ta MUNOSCO ta ce bayan musayar wuta tsakanin sassan biyu a karshen mako, yanzu bangarorin biyu suna amfani da kananan makamai kamar rokoki.

Tawagar ta MONUSCO ta kuma nanata kiran da ta yi na kai zuciya nesa kuma dakarunta da ke yankin na zaman shirin ko ta-kwana.

A ranar Jumma'a, kakakin MDD ya bayyana cewa, an dakatar da fada tsakanin dakarun gwamnati da 'yan tawayen kungiyar M23 a kusa da garin Kanyaruchinya, kimanin kilomita 15 daga Goma, babban birnin lardin arewacin Kivu.

Nesirky ya kuma bayyana cewa, MONUSCO ta girke dakarunta cikin shirin kota-kwana, tun lokacin da fadan ya barke a ranar 14 ga watan Yuli, kuma a shirye ta ke ta dauki dukkan matakan da suka dace, ciki har da amfani da karfi wajen kare fararen hula.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China