in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da cikakken zama na 37 na kwamitin gwamnatoci mai kula da sauye-sauyen yanayi na MDD
2013-10-15 09:28:51 cri
An kaddamar da cikakken zama na 37 na kwamitin gwamnatoci mai kula da sauye-sauyen yanayi na MDD wato IPCC a birnin Batumi dake kasar Georgia a jiya ranar 14 ga wata. An shafe kwanaki 5 wajen gudanar da taron, kuma wakilai fiye da 250 daga hukumomin gwamnatoci da bangaren fasaha na kasashe 110 suka halarta. A lokacin taron, wakilan za su kara tattaunawa kan sabbin abubuwan dake cikin rahoton bincike na 5 game da sauye-sauyen yanayi da kwamitin IPCC ya gabatar a birnin Stockholm na kasar Sweden a watan da ya gabata.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, za a kammala tattaunawa, kuma za a gabatar da dukkan abubuwan dake cikin rahoton bisa makatai daban daban kafin watan Oktoba na shekarar 2014. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China