in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a jinkirta yanke hukunci ga shugabannin Afirka dake kan mulki, in ji shugaban Afirka ta Kudu
2013-10-14 20:23:47 cri
A ranar Litinin 14 ga wata, shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma ya bayyana cewa, kasarsa tana goyon bayan bukatar da kungiyar AU ta mika wa kotun manyan laifukan duniya ta jinkirta yanke hukunci ga shugabannin kasashen Afirka dake kan mulki.

Shugaba Zuma ya ce, yanzu bai kamata a yanke hukunci ga shugabannin kasashen Afirka dake kan mulki ba amma za a iya yanke musu hukunci bayan kammala wa'adin mulkinsu. Idan kuma har sun aikata laifi, ya kamata a jinkirta yanke musu hukunci, ta yadda za su kammala aikinsu yadda ya kamata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China