in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi jerin gwanon nuna goyon baya ga gwamnatin Nijar gabanin tattaunawa da kamfanin Areva
2013-10-13 16:18:53 cri
Wani gungun kungiyoyin fararen hula na birnin Arlit dake arewacin kasar ya gudanar da wani taron gangami tare da jerin gwano a ranar Asabar domin nuna goyon baya ga gwamnatin Nijar dake shirin tattaunawa kwanaki masu zuwa kan farashin sinadarin uranium tare da kamfanin Areva na kasar Faransa in ji daya daga cikin shugabannin wannan taron gangami a cikin hirarsa da wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua dake Niamey.

Gwamnatin Nijar dai da abokin kasuwacinsa na Areva dake hakar ma'adinan uranium tun yau da kusan shekaru hamshin a arewacin kasar, za ta sake tattauna kwangilar dake tsakaninta da Areva yau da kusan shekaru goma domin ganin ta cimma wata sabuwar kwangila cikin dogon lokaci tare da wannan kamfani na kasar Faransa da za ta kasance mafi alfanu ga kasar Nijar. Hukumomin kasar Nijar na ganin cewe babu daidaici kan huldar kasuwancinta tare da Areva, lamarin dake nuna cewa kasar Nijar bata samun wata babbar moriya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China