in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hare-haren bom a arewacin Jamhuriyar Nijar
2013-05-23 20:58:21 cri
A ranar Alhamis din nan da sassafe ne, aka kai hari da boma-bomai a wani sansanin soja da kuma wani kamfanin hakar ma'adinan Uranium dake arewa maso yammacin Jamhuriyar Nijar.

Wani mutum da ake kyautata zaton dan kunar-bakin-wake ne ya tayar da bom a wani barikin soja dake birnin Agadez, abun da ya sa wanda ya jefa bom ya mutu nan take, sa'an nan mutane da dama suka jikkata. Ministan tsaro na Jamhuriyar Nijar Mahamadou Karidjo ya ce, sojoji a kalla 17 ne suka rasa rayukansu.

A can birnin Arlit ma, rahotanni na cewa yau da misalin karfe 5 da rabi na safe, wasu bama-bamai sun tashi a kamfanin Somair mai hakar ma'adanin Uranium mallakar kasar Faransa, lamarin da ya raunata mutane 13. A halin yanzu dai ma'aikatan ceto na Jamhuriyar Nijar sun isa gurin domin gudanar da ayyukin ceto

Wadannan boma-bomai sun tashi ne kusan a lokaci guda.

Har wa yau kuma, ministan tsaro na kasar Nijar Mahamadou Karidjo, ya ce ana kyautata zaton mutanen da suka kai hare-haren kunar-bakin-waken suna da alaka da kungiyar Al-Qaeda, kuma watakila sun shigo kasar ce daga kudancin kasar Libya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China