in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya isa birnin Jakarta domin ziyarar aiki
2013-10-02 16:12:01 cri

A laraban nan 2 ga watan October Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa Jakarta babban birnin kasar Indonesia domin fara ziyarar aiki ta farko da zai kai kasashen kudu maso gabashin nahiyar Asiya tun darewar sa karagar mulkin kasar a watan Maris din bana.

A lokacin ziyarar tasa a Indonesia,Shugaba Xi zai gana da takwaransa Susilo Bambang Yudhoyono da kuma mataimakin Shugaban kasar Boedijono da shugabanni majalissar dokokin kasar sannan kuma zai halarci liyafar cin abinci da wasu manyan 'yan kasuwa.

Kasashen biyu sun cimma nasarori tare wajen hadin gwiwa a bangaren kimiyya da fasasha,ilimi,al'adun gargajiya,musanyan jama'ar su, tsaro da kariya, sufurin jiragen ruwa da na jiragen sama.

Bayan kammala ziyarar sa a Indonesia, Shugaba Xi zai ziyarci kasar Malaysia daga baya kuma ya sake komawa Indonesian domin halartar taron shugabannin kasashe membobin Kungiyar habaka tattalin arzikin nahiyar Asiya da yankin tekun Pacific wato APEC da za'a yi daga ranar 7 zuwa 8 ga watan na Oktoba. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China