in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya kai ziyara Malaysia
2013-10-03 20:47:25 cri
A daren ranar Alhamis 3 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Kuala Lumpur domin fara ziyarar aiki a kasar Malaysia.

Shugaba Xi ya tashi daga birnin Jakarta zuwa na Kuala Lumpur bayan kammala ziyararsa a Indonesiya.

A yayin da yake ziyara a Malaysia, shugaba Xi zai gana tare da yin shawarwari da shugaban kasar, Abdul Halim Mu'adzam Shah, da firaministan kasar, Najib Razak, tare da halartar taron koli kan tattalin arziki.

A cikin 'yan shekarun da suka wuce, ci gaban dangantaka tsakanin Sin da Malaysia yana da kyau, kuma an sami ci gaba sosai wajen hadin gwiwa tsakaninsu a fannoni daban daban.A bara jimillar kudin cinikayya tsakanin bangarorin biyu ta kai dala biliyan 94.8, har ma Sin ta kasance aminiyar Malaysia a fannin cinikayya mafi girma a duniya cikin shekaru hudu a jere, yayin da Malaysia ta zama aminiyar Sin a fannin cinikayya mafi girma a kungiyar kasashen kudu maso gabashin Asiya cikin shekaru biyar a jere.

Malaysia ta kasance kasa ta biyu da shugaba Xi ya ziyarta a yankin kudu maso gabashin Asiya a wannan karo. Daga bisani kuma, shugaba Xi zai tashi zuwa tsibirin Bali na Indonesiya, domin halartar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 21 da za a yi a wurin.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China