in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dalibai da dama sun mutu a wani harin da aka kai wata makaranta a jihar Yobe ta Nijeriya
2013-09-29 20:28:19 cri
A safiyar ranar Lahadin nan 29 ga wata wassu dalibai da dama suka rasa rayukansu a wani harin da aka kai wata makarantar gaba da sakandare a jihar Yobe dake arewa maso gabashin kasar wanda kuma ake zaton 'yan kungiyar nan ne ta Boko Haram suka kai shi.

An kai ma kwalejin ilimin aikin gona dake Gujba mai nisan kilo 50 daga Damaturu babban birnin jihar Yobe harin ne lokacin da wassu 'yan bindiga suka fara harbi ta ko ina, abin da ya yi sanadiyar harbe dalibai da dama har lahira.

Wata majiya ta shaida ma wakilin Xinhua cewa an samu gawawwaki da dama a cikin dazukan kewayen makarantar, dakunan daukar darasi da kuma dakunan kwana daliban dake ciki da wajen makarantar, kuma har a lokacin da labarin ya iso mana nan, majiyar ta tabbatar da ana kan tsinto wassu gawawwakin da kuma ceto wadanda suka ji rauni.

Jami'an tsaro dai ba su kai ga tabbatar da labarin ba ko kuma adadin wadanda wannan harin ya rutsa da su a lokacin da labarin ya iso mana. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China