in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta sake nanata cewa za ta dauki matsayin ba ruwanta kan batun tsibirin Diaoyu
2013-09-18 20:15:26 cri
A kwanan baya, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amurka Jen Psaki ta sake bayyana cewa, Amurka za ta dauki matsayin ba ruwanta kan batun mallakar tsibirin Diaoyu. Game da wannan batu kuma, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin Hong Lei ya bayyana a ranar Laraba 18 ga wata a nan birnin Beijing cewa, ana fatan Amurka za ta cika alkawarinta, ta gudanar da ayyuka cikin taka-tsamtsam, a kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyya-shiyya da kuma dangantaka tsakanin Sin da Amurka.

Mr. Hong ya jaddada cewa, tun asali daman kasar Sin take da mallakar tsibirin Diaoyu da wasu tsibiran dake kewayensa, a bayyane yake cewa Sin ta nuna matsayinta kan batun tsibirin.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China