in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na da aniya da kwarewar kiyaye ikon mulkin kasa a tsibirin Diaoyu
2013-01-21 20:31:58 cri
Dangane da furucin da ma'aikatar harkokin wajen kasar Japan ta yi na cewa, bunkasuwar rundunar kasar Sin na sauya yanayin tsaro a wannan yankin da take ciki, kuma Sin tana kokarin canza odar da ake bi a yanzu, Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a ranar 21 ga wata a nan Beijing cewa, har kullum kasar Sin a tsaye take tsayin daka kan adawa da ayyukan da Japan take yi na keta ikon mulkin kasar Sin a tsibirin Diaoyu da tekun da ke kewaye da shi.

Mista Hong ya kara da cewa kasar Sin na da aniya da kuma kwarewar kiyaye ikon mulkin kasa a tsibirin na Diaoyu.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China