in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya tattauna da takwaransa na Rasha
2013-09-18 10:01:09 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, zanta da takwaransa na kasar Rasha Sergei Lavrov ta wayar tarho a daren jiya Talata, inda suka yi musayar ra'ayoyi sosai kan batun kasar Syria.

A yayin tattaunawar, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin ta yi maraba sosai ga shirin yarjejeniyar da kasashen Rasha da Amurka, suka cimma game da batun makamai masu guba na Syria, tana kuma fatan za a aiwatar da abubuwan dake cikin yarjejeniyar.

Bugu da kari Wang Yi ya ce, kasar Sin na ganin cewa, ba za a iya warware matsalar da kasar Syria ke fuskanta, ta hanyar daukar matakin soja ba. Yace Kasar Sin na fatan ci gaba da taka muhimmiyar rawa, a fagen inganta yunkurin da ake yi na warware matsalar Syria a siyasance.

A nasa bangaren, Lavrov ya amince da wannan matsayi na kasar Sin. Bugu da kari bangarorin biyu sun amince da ci gaba, da yin hadin gwiwa tsakaninsu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China