in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin na bukatar kasashen duniya da su kawar da ra'ayin siyasa da raba kafa kan hakkin dan Adam
2012-11-09 14:34:00 cri
A ran 8 ga wata, mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Wang Min, ya bayyanawa mambobin zauren MDD a birnin New York, hedkwatar majalisar cewa, ya kamata gamayyar kasa da kasa su kawar da ra'ayin siyasa da matakin raba kafa kan batun hakkin dan Adam, tare kuma da karfafa musaya da hadin gwiwa kan batun, ta yadda za a iya dakile kalubalen da ake fuskanta a wannan fanni.

A yayin taron kwamiti na uku na MMD mai kula da harkokin zamantakewa, mutuntaka da al'adu, na babban taron MDD karo na 67 kan batun hakkin dan Adam, Mr. Wang Min ya nuna cewa, wasu kasashe na son sukar kasashe masu tasowa kan batun hakkin dan Adam, ta yadda suke kutsa kai cikin harkokin gida na wadannan kasashe, matakin da ke nuni ga karya ka'idojin MDD.

Wang Min ya jadadda cewa, kamata ya yi gamayyar kasa da kasa su mai da hankali kan kyawawan manufofin zaman rayuwa, da ikon samar da cigaba na kasashe masu tasowa, da kuma cika alkawarinsu na ba da taimako ga kasashen, bai kamata su yi ta suka kan batun hakkin dan Adam a kasashe masu tasowa ba.

Wang Min ya kuma yi kira ga gamayyar kasashen duniya, da su kau da ko wane irin rainin da suke nunawa. Ya ce, a kwanakin baya, zanga-zangar nuna rashin jin dadi daga bangarori daban daban ta rika tashi, sabo da wani fim da ya yi batanci ga addinin musulunci, kasar Sin ta mai da hankali sosai kan wannan batu, sabo da Sin na kin yarda da dukkanin manufofin da suka bata mutuncin addinin musulunci, bugu da kari, ya zama dole ga kasashen duniya, da su nuna kiyayya ga duk wani nau'in nuna wariyar kabila. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China