in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin CADHP zai yi bikin cikon shekaru 25 da kafurwa a kasar Cote d'Ivoire
2012-10-07 17:43:58 cri
Kwamitin kare hakkin da adam da al'ummomi (CADHP) zai bikin cikon shekaru 25 da kafuwarsa a mako mai zuwa a Yamoussoukro, hedkwatar kasar Cote d'Ivoire a albarkacin wani zaman taronsa karo na 52 da za'a shirya.

A ranar Talata, shuagaban Cote d'Ivoire, Alassane Ouattara zai halarci bikin bude taro da zai kwashe makonni biyu, da kuma zai karbi wakilan kungiyoyi masu zaman kansu 500 bisa taken "kwamitin Afrika kan kare hakkin dan adam da al'ummomi, shekaru 25 kan kokarin bunkasa da kiyaye hakkin dan adam a Afrika".

Ministan kare hakkin dan adam da 'yancin jama'a na kasar Cote d'Ivoire, ya bayyana cewa burin farko na wannan dandali shi ne na maido da martabar kasar Cote d'Ivoire game da batun kare hakkin dan adam, bayan tashe tashen hankalin siyasa da suka janyo babbar illa ga 'yancin dan adam a kasar.

Wannan haduwa ta Yamoussoukro za ta kasance tare da wasanni da za'a nunawa jama'a kan 'yancin dan adam da kuma mahawarori kan wannan batu, kuma shugabar wannan kwamiti, Catherine Dupe Atoki ta isa birnin Yamoussoukro tun ranar Jumm'a. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China