in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Obama na ci gaba da neman goyon baya kan daukar matakan soja ga Syria
2013-09-09 11:02:07 cri
A sakamakon rashin cikakken goyon bayan al'ummarta kan daukar matakan soja kan Syria, gwamnatin Obama na fuskantar matsala daga majalisar dokoki a wannan yunkurin nata. Don neman karin goyon baya, Mr. Barrack Obama a wannan mako na shirin daukar wasu matakai na tuntubar jama'a. A sa'i daya kuma, gamayyar kasar da kasa na ci gaba da ja-in-ja dangane da rikicin da ke faruwa a Syria.

An ce, a ranar 9 ga wata, shugaba Obama zai tattauna da 'yan jarida na wasu manyan gidajen talabijin na kasar, inda zai bayyana muhimmancin daukar matakan soja kan Syria don hukunta gwamnatin kasar da aka zargin ta yi amfani da makamai masu guba, zai kuma yi alkawarin kayyade tsawon lokacin daukar matakan soja. Sai kuma a ranar 10 ga wata, Obama zai yi wani jawabi ga al'ummar kasar baki daya ta gidan talabijin, inda zai sake jaddada muhimmancin daukar matakan soja kan Syria da kuma ma'anarsa ta bangaren kiyaye moriyar Amurka, don sassauta damuwar jama'ar kasar da ke kin yarda da yakin.

A sa'i daya, a ranar 7 ga wata, sakataren harkokin waje na kasar Amurka, John Kerry ya isa Faransa, inda ya samu goyon baya daga gwamnatin kasar, sai dai a cewar gwamnatin Faransa, za ta jira har zuwa lokacin da masanan MDD kan makamai masu guba suka fitar da rahoton bincikensu, kuma ta fi son warware matsalar Syria ta hanyar siyasa.

Har ila yau, shugabar gwamnatin kasar Jamus, Angela Merkel ta bayyana a ranar 8 ga wata, inda ta ce, Jamus tana kokarin ganin kwamitin sulhun MDD ya dauki matakai na bai daya. Ta jaddada cewa, dole ne a daidaita matsalar Syria a siyasance, kuma Jamus ba za ta shiga aikin soja da ake son aiwatarwa ba.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China