in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a nemi iznin kwamitin sulhun MDD kafin daukan matakin soja kan Syria, in ji shugaban Rasha
2013-09-04 16:03:08 cri
A jiya Talata 3 ga wata ne, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayyana cewa, yau ne ake sa ran samfurin sinadarai da aka tattara, daga wurin da ake zargin an kaddamar da hari da makamai masu guba a kasar Sham ko Syria, za su isa dakunan gwaje-gwaje da aka tanada don yin nazari.

A sa'i daya kuma ya jadadda cewa, ya kamata a nemi iznin kwamitin sulhu na MDD kafin a dauki ko wane irin matakin soja kan zargin yin amfani da makamai masu guba da akewa mahukuntan kasar.

Don gane da wannan batu shi ma shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya bayyana a yau din nan cewa, ya kamata a nemi iznin kwamitin sulhu na MDD, kafin a dauki matakan soja a Syria, yana mai cewa, ko wane irin matakin soja da za a dauka kan Syria ba tare da iznin MDD, na iya zama yakin da ba shi da goyon bayan doka wato hari ne. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China