in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata kasashen da abin ya shafa su mai da hankali sosai kan batun daukar matakan soja a Syria, in ji kasar Sin
2013-09-06 14:56:33 cri
Ran 5 ga wata, yayin taron shugabannin G20 da aka yi a birnin Saint Peterburg, kakakin tawagar wakilan Sin Qin Gang ya bayyana cewa, idan har aka dauki matakan soja kan kasar Syria ba tare da amincewar kwamitin sulhu na MDD ba, hakan zai haifar da illa ga kasar ta Syria, dama yankin Gabas ta tsakiya baki daya, shi ya sa kasar Sin ke yin kira ga kasashen da abin ya shafa, da su yi taka tsan tsan sosai kan batun daukar matakan soja a kasar ta Syria.

Yayin taron manema labaran da cibiyar watsa labaran tawagar wakilan kasar Sin ta kira, Qin Gang ya nuna cewa, kasar Sin ta damu matuka kan halin da kasar Syria take ciki a yanzu. Kuma Sin ba ta amincewa ko wace kasa, ko wata kungiya, ko wane mutum ya yi amfani da makamai masu guba. Abu mafi muhimmanci a halin yanzu shi ne, MDD ta dukufa wajen yin bincike kan zargin amfani da makamai masu guba, ta yadda za a iya gano gaskiya, kafin daukar ko wane irin mataki a nan gaba.

Qin Gang ya kuma kara da cewa, ba za a iya warware matsalar da ake fama da ita ta hanyar yaki ba. Ya ce a halin yanzu ya kamata kasashen duniya su dukufa matuka wajen dakile tashe-tashen hankula a kasar Syria, tare da kuma ba da taimako wajen aiwatar da sauyin siyasa a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China