in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
sabunta: An rantsar da Ibrahim Boubacar Kaita a matsayin sabon shugaban kasar Mali
2013-09-04 20:16:04 cri
A safiyar yau laraba 4 ga wata a Bamako babban birnin kasar Mali aka yi bikin rantsar da sabon Shugaban kasar Ibrahim Boubacar Keita, a zauren taro na kasa da kasa dake Bamako da Mambobin babban kotun kasar suka shaida.

Bikin rantsarwar dai ya zo makonni biyu bayan sanar da samun nasarar babban zabe da aka jefa zagaye na biyu a ranar 11 ga watan jiya na Agusta kamar yadda kotun tsarin mulki na kasar ta shirya bisa doka mai lamba 37 na kundin tsarin mulkin.

A lokacin sanar da sakamakon zaben zagaye na karshe da aka yi a ranar 20 ga watan na Agusta Shugaba kotun tsarin mulkin kasar Amadi Tamba Camara ya sanar da sunan Ibrahim Boubacar Keita a matsayin zababben Shugaban kasa wanda ya samu kashi 77.62 a cikin 100 na kuri'un da aka jefa abinda yasa ya doke abokin hamayar sa Soumaila Cisse wanda ya samu kashi 22.38 a cikin 100 na kuri'un. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China