in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Samun nasarar zaben shugaban kasar Mali, muhimmin mataki ne a fannin maido da dimokuradiyya da oda a kasar
2013-08-17 15:59:42 cri
Ranar 16 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya ba da wata sanarwa, inda ya yaba wa kasar Mali game da samun nasarar gudanar da zaben shugaban kasar, kuma a ganinsa, wannan shi ne muhimmin mataki na maido da tafiyar da harkokin kasa ta hanyar dimokuradiyya da sake samun oda da tsarin mulkin kasa a kasar ta Mali.

Madam Maria Cristina Perceval, shugabar kwamitin sulhu ta wannan wata kuma zaunanniyar wakiliyar kasar Argentine a MDD ta karanta wannan sanarwa.

Dangane da batun arewacin kasar Mali, kwamitin sulhu ya yi kira ga bangarori masu ruwa da tsaki da su aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka daddale a watan Yuni na bana a birnin Ouagadougou, hedkwatar kasar Burkina Faso, su kuma yi shawarwarin zaman lafiya da bangarori daban daban za su iya shiga da amincewa cikin lokacin da yarjejeniyar ta tsara, inda za su lalubo bakin zaren daidaita rikicin kasar ta hanyar siyasa cikin dogon lokaci, ta yadda za a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali cikin dogon lokaci a sassa daban daban na Mali.

Har wa yau kuma, kwamitin sulhu ya yi kira ga Mali da ta gudanar da zaben 'yan majalisar kasar cikin hanzari, tare da tabbatar da 'yancin kai, da adalci ba tare da boye kome ba. Sa'an nan kwamitin sulhu ya jaddada muhimmancin yin shawarwari da samun sulhu a duk fadin kasar ta Mali. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China