in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka na daf da daukar matakan da suka dace don gane da rikicin kasar Sham
2013-08-24 17:07:32 cri
Shugaba Barack Obama na Amurka ya ce, shirye-shirye sun yi nisa, a kokarin da kasarsa ke yi na daukar matakan kawo karshen fadace-fadacen dake wakana a kasar Sham.

Cikin wani jawabin da ya gabatar a ranar Jumma'a, shugaba Obama ya ce, rundunar sojin kasarsa na tattara bayanai kan batun kai hari da makamai masu guba da aka aiwatar a wajen birnin Damascus na kasar Sham, da nufin daukar dukkanin matakan da suka dace.

Bugu da kari, shugaban na Amurka ya ce, kasarsa na ci gaba da matsin lamba ga MDD, domin ganin an aiwatar da shirye-shiryen kare fararen hula daga hare-haren dake aukuwa, sakamakon yakin basasar kasar ta Sham. A sa'i daya kuma Amurka za ta tabbatar da hana yaduwar makamai masu guba a kasar.

Sai dai yayin da yake amsa tambayar wata kafar yada labarai, shugaba Obama ya nuna dari-dari ga batun kaiwa wata kasa hari, ba tare da cikakken goyon bayan MDD ba. Yana mai cewa, daukar irin wannan mataki na iya jefa shakku ga batun kiyaye dokokin kasa da kasa.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China