in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nahiyar Afirka za ta kafa yankin ciniki cikin 'yancin a shekara ta 2015
2013-08-20 20:45:12 cri
Shugaban kasar Afirka ta kudu Jacob Zuma, ya fada a ranar Litinin cewa, ana sa ran kasashen Afirka za su kafa yankin da za a gudanar da ciniki cikin 'yancin a shekara ta 2015,ganin yadda nahiyar ke da yawan al'ummar da ta kai kimanin miliyan 600 da yawan GDP da ya kai dala triliyan 1, idan aka hade kasuwannin kasashe 26 na nahiyar waje guda.

Shugaba Zuma ya shaidawa mahalarta taron majalisar 'yan kasuwar kungiyar kasahen BRICS na farko a birnin Johannnesburg cewa,abu mai muhimmanci shi ne, wannan mataki zai taimaka wajen samar da yankin da za a rika gudanar da ciniki cikin 'yanci a nahiyar,tsarin da zai kai ga samar da kasuwa bai daya da kudin da ya kai dala triliyan 22.6.

Zuma ya ce wannan mataki zai taimakawa kasashen Afirka su kara bunkasa harkokin cinikayya a nahiyar,ya kuma bayyana cewa,kasashen na Afirka karkashin kungiyar AU, za su bullo da yankin ciniki cikin 'yanci,inda za su hada kan kasashen gabashi da na kudancin Afirka waje guda.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China