in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardan MDD ya yi kiran lafa kura a Masar
2013-08-18 16:39:10 cri
A ranar asabar magatakardan MDD Ban Ki Moon yayi kira ga masu zanga zanga da mahukunta a kasar Masar dasu yi hakuri su kuma yi kokarin lafa kura.

Wata sanarwa da mai Magana da yawun magatakardan na MDD ya bayar na mai bayyana cewa Magatakardan ya damu matuka dangane da abubuwa dake aukuwa a kasar Masar da kuma bazuwar barkewar rikici kana da amfani da karfin tuwo wajen shawo kansu.

Cikin sanarwar Mr Ban yayi suka da kakkausar murya kan harin da aka kai a majami'u, asibitoti da sauran wuraren jama'a inda yace ko kadan hakan bai dace ba. (Lami Ali Mohammed)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China