in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya gana da mahalarta taron ministocin kasashen Sin da Afirka game da hadin gwiwa da raya aikin kiwon lafiya
2013-08-16 19:56:07 cri
Ranar 16 ga wata, a nan Beijing, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya gana da wakilan mahalarta taron ministocin kasashen Sin da Afirka game da hadin gwiwa da raya aikin kiwon lafiya.

A yayin ganawar, shugaba Xi ya bayyana cewa, yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka ta fuskar kiwon lafiya, wani muhimmin bangare ne na hadin gwiwar da ke tsakaninsu. Yana fatan taron zai ba da gudummowa wajen kara azama kan yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka a fannin kiwon lafiya, da tabbatar da lafiyar jama'ar Sin da Afirka, bisa tsarin taron dandalin tattaunawar yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka.

Har wa yau shugaban ya nuna godiya kan gudummowar da kungiyoyin kasa da kasa suka bayar kan goyon bayan ayyukan kiwon lafiya na Sin da Afirka, da tabbatar da adalci a duk duniya ta fuskar kiwon lafiya. Ya kuma bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da mara musu baya, da kuma goyon bayan kasashen Afirka da su tabbatar da manufar bunkasuwa da MDD ta tsara a shekarar 2000 wato MDGs cikin sauri. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China